fidelitybank

Shari’u sun yi wa kotun koli yawa – Alkalin Alkalai Ariwoola

Date:

Alƙalin alƙalan Najeriya, mai shari’a Olukayode Ariwoola, ya ce, shari’o’i sun yi wa kotun ƙolin ƙasar yawa, ciki kuwa har da waɗanda ba su taka kara sun karya ba.

Babban mai shari’ar ya bayyana haka ne a Abuja, lokacin wani taro na musamman na ƙaddamar da shekarar shari’a ta 2022 zuwa 2023, da kuma rantsar da manyan lauyoyi 63 na ƙasar.

A cewar alƙalin wasu daga cikin shari’o’in ba su cancanci a kai su kotun ta ƙoli ba.

Ya ce “akwai buƙatar a tunatar da ƴan Najeriya cewar ya kamata su daina yawan shigar da ƙararraki, a maimakon haka, su rinƙa bin wasu hanyoyin sulhuntawa domin rage wa kotuna nauyi.”

Ya ƙara da cewa “ƴan Najeriya, musamman ma ƴan siyasa ne waɗanda suka fi shigar da ƙara a faɗin duniya.”

A lokacin da yake bayani kan alƙaluma, mai shari’a Ariwoola ya ce akwai ƙararraki 6,884 da aka ɗaukaka zuwa kotun ƙoli waɗanda ba a yi aiki a kansu ba har yanzu.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp