fidelitybank

Shafi Mulera: Ku daina ɗaukar doka a hannu – Jami’an Tsaro

Date:

Rundunar ƴan sandan Babban birnin tarayya, ta gargaɗi mazauna yankin kan ɗaukar doka a hannu kan waɗanda ake zargi da aikata laifuka, domin gudun tayar da zauna tsaye.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hannun jami’arta ta yaɗa labaru da hulɗa da jama’a, SP Josephine Adeh, ta ce ta yi gargaɗin ne bayan yunƙurin da wasu mutane suka yi na hukunta wani mutum da aka zarga da satar al’aura a yankin Karshi na babban birnin tarayyar.

Sanarwar ta ce, lamarin ya faru ne a ranar Asabar ɗin da ta gabata, inda wasu maza uku suka ce sun ji wani yanayi da ba su gane ba a al’aurarsu bayan haɗa jiki da mutumin.

Bayan hakan ne dandazon mutane suka far wa wanda ake zargin, sai dai jami’an ƴan sanda sun ceci shi sa’ar da suka isa wurin, jim kaɗan bayan bayan fara ɗaukar matakin.

Dalilin haka ne kwamishinan ƴan sanda na yankin birnin tarayyar, CP Haruna G. Garba ya buƙaci jama’a da su guji ɗaukar irin wannan mataki.

A cikin kwanakin nan an riƙa yaɗa labaru, waɗanda ba a tantance ba kan ɓullar mutane masu satar al’aura bayan haɗa jiki ko kuma shan hannu da al’umma.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp