Matsalolin da ke addabar jam’iyyar PDP sun ƙara tsananta a ranar Lahadi, bayan ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya janye daga duk wata yarjejeniya ta sulhu da aka taba cimmawa a cikin jam’iyyar adawar.
Wike dai ya ɗora alhakin rikicin PDP a kan gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, yana mai gargaɗin cewa rashin bin yarjejeniyoyin da aka cimma ne ke haddasa rikicin jam’iyyar, kuma ya bayyana Makinde a matsayin wanda ya fi haddasa wannan matsala.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, Wike ya zargi manyan shugabannin jam’iyyar, ciki harda gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, da cin amanar juna da rashin gaskiya da kuma karya yarjejeniyoyi da dama da aka cimma a baya.
Yayin da yake bayani kan asalin rikicin PDP tun bayan kammala zaɓen 2023, Wike ya zargi Makinde da gurɓata dukkan ƙoƙarin sasanci da zaman lafiya a cikin jam’iyyar.