Kungiyar Kare Hakkokin Tattalin Arziki ta (SERAP), ta yi Allah-wadai da cire albashin mambobin kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) daga watan Oktoba.
Kungiyar ta bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya umurci ministan kwadago Chris Ngige da mukaddashin Akanta Janar Sylva Okolieaboh da su janye kudaden da aka cire.
SERAP ta kuma bukaci mambobin kungiyar ASUU su samu cikakken albashi na tsawon watanni takwas da suka yi na yaƙin aiki.
A wata budaddiyar wasika, mataimakin darakta Kolawole Oluwadare, ya ce, kudaden da aka cire sun hada da hukunta malaman da suka yi na yajin aiki.
Kungiyar ta ce, wannan rabe-raben ya saba wa ‘yan kungiyar ASUU na samun isasshiyar rayuwa ga kansu da iyalansu.