fidelitybank

SERAP ta maka Akpabio da Tajudeen a gaban kotu

Date:

A yayin da ake ta cece-kuce, kungiyar kare hakkin al’umma da tattalin arzikin kasa (SERAP), ta shigar da karar shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, kan kin kawo karshen ayyukan da ba bisa ka’ida ba na kayyade alawus-alawus na ‘yan majalisa da kudin tafiyar da su.

Kolawole Oluwadare, Mataimakin Daraktan SERAP ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

A cewar SERAP, an shigar da karar ne a ranar Juma’ar da ta gabata a babbar kotun tarayya da ke Abuja mai lamba FHC/ABJ/CS/1289/2024.

SERAP ta ce, “Odar mandamus na umurtar da tilasta Mista Akpabio da Mista Abbas su bayyana ainihin adadin kudaden gudanar da ayyukan da ‘yan majalisar ke biya da kuma karban duk wata, da kuma bayanan kashe kudaden gudanar da ayyukan,” in ji SERAP.

Kungiyar ta kara da cewa “Tattalin da sakin layi na N, sashe na 32 (d) na Jadawali na Uku ga Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 [kamar yadda aka gyara] ya haramtawa Majalisar Dokoki ta kasa gyara ma’aikata albashi, alawus-alawus da kudaden tafiyar da ayyukanta.”

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ya yi zargin cewa ‘yan majalisa na gyara albashi da alawus-alawus dinsu, sabanin shawarar hukumar tattara kudaden shiga (RMAFC).

Ko da yake an fayyace cewa Sanatoci 109 a Najeriya suna karbar albashin N1,063,860 duk wata, amma bai bayyana adadin alawus-alawus din ba.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Sanatan Kano ta Kudu, Abdurrahman Kawu Sumaila ya ce Sanatoci na samun Naira miliyan 21 a duk wata.

Shehu Sani, wanda tsohon Sanata ne, ya ce ikirarin Sumaila kan kudin gudanar da aiki ya tabbatar da shi.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp