Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa, yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da ke yin katsalandan da sunan addinin Musulunci ya kusa kawo karshe kuma “Nasara tana nan za a gani”.
Shugaban ya bayar da wannan tabbacin ne a cikin sakonsa na Sallah ga ‘yan Najeriya yayin da watan Ramadan ke karatowa, kuma Musulmi za su gudanar da bikin Eid-el-Fitr a hukumance a ranar Litinin.
Mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Malam Garba Shehu, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce, shugaban ya aika sakon fatan alheri ga al’ummar Musulmi a Najeriya da ma duniya baki daya da suke murnar wannan rana.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Yayin da watan Ramadan ke karewa, kuma Musulmi suka gudanar da bukukuwan Sallah, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika sakon gaisuwar sa ga Musulman Najeriya da ma duniya baki daya da suke murnar zagayowar wannan rana.