fidelitybank

Sauyin Kudi: Buhari da Emefiele na wasa da hankalin ‘yan Najeriya – Sowore

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar African Action Congress, AAC, Omoyele Sowore a ranar Laraba, ya caccaki shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele, kan sabbin takardun kudi na naira da aka yi wa kwaskwarima.

Sowore ya zargi Buhari da Emefiele da wasa da ‘yan Najeriya ta hanyar sake fasalin Naira.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, dan takarar shugaban kasa na AAC ya bayyana shugaban kasar da gwamnan CBN a matsayin ‘yan damfara.

Ya kuma jaddada cewa babu wani gagarumin sauyi da ya samu kan Naira, kuma da alama an sake yaudarar ‘yan Najeriya.

Buhari ya kaddamar da sabbin takardun kudi na N200, N500 da kuma N1000 a yayin fara taron mako na majalisar zartarwa ta tarayya (FEC).

Sabbin takardun Naira za su fara aiki ne daga ranar 15 ga watan Disamba, yayin da tsofaffin za su daina aiki daga ranar 1 ga Fabrairu, 2023.

Wannan shi ne karon farko cikin shekaru 19 da Najeriya za ta sake fasalin wasu takardun kudinta.

Da yake raba hoto a shafin Twitter, Sowore ya nuna rashin jin dadinsa game da ci gaban.

Ya rubuta: “@GodwinIemefiele na bankin @cenbank, kuma @MBuhari dai ya yi wa ‘yan Najeriya wasa kan zamba da ake kira sake fasalin Naira. Babu wani abu da aka “sake fasalin” kawai canjin rini. ‘Yan damfara! #Bazamu Cigaba Kamar Wannan ba.”

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...
X whatsapp