fidelitybank

Sauya jam’iyya: Ranar 11 ga watan Afiliru Yakubu Dogara zai san makomar sa

Date:

A ranar 11 ga watan Afrilu ne dai aka sanya ranar shari’ar da ake yi na neman korar tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara kan sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.

Jam’iyyar PDP da shugabanta na jihar Bauchi Hamza Akuyam ne suka shigar da karar a gaban mai shari’a Donatus Okorowo na wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a shekarar 2020.

Dogara ya wakilci mazabar Dass, Tafawa Balewa da Bogoro na jihar Bauchi a majalisar wakilai.

Jam’iyyun da ke cikin karar sun hada da Shugaban Majalisar Wakilai, Babban Lauyan Tarayya (AGF), Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da kuma Jam’iyyar APC.

Jam’iyyar PDP ta yi zargin cewa tsohon shugaban majalisar, a karkashin sashe na 68 (1) (g) na kundin tsarin mulkin kasar, bai cancanci zama majalisar wakilai ba bayan ya yi watsi da jam’iyyar PDP, wadda a kan dandalin ta ya ci zaben sa a 2019.

Kimanin makonni biyu da suka gabata mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya kori gwamna David Umahi na jihar Ebonyi da mataimakinsa Kelechi Igwe da kuma wasu ‘yan majalisar dokokin jihar su 15 da suka sauya sheka daga PDP zuwa APC.

A ranar Litinin din da ta gabata ne, mai shari’a Taiwo Taiwo na wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ya kori ‘yan majalisar dokokin jihar Cross River su 20 saboda sauya sheka daga PDP zuwa APC.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp