A ranar 11 ga watan Afrilu ne dai aka sanya ranar shari’ar da ake yi na neman korar tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara kan sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.
Jam’iyyar PDP da shugabanta na jihar Bauchi Hamza Akuyam ne suka shigar da karar a gaban mai shari’a Donatus Okorowo na wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a shekarar 2020.
Dogara ya wakilci mazabar Dass, Tafawa Balewa da Bogoro na jihar Bauchi a majalisar wakilai.
Jam’iyyun da ke cikin karar sun hada da Shugaban Majalisar Wakilai, Babban Lauyan Tarayya (AGF), Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da kuma Jam’iyyar APC.
Jam’iyyar PDP ta yi zargin cewa tsohon shugaban majalisar, a karkashin sashe na 68 (1) (g) na kundin tsarin mulkin kasar, bai cancanci zama majalisar wakilai ba bayan ya yi watsi da jam’iyyar PDP, wadda a kan dandalin ta ya ci zaben sa a 2019.
Kimanin makonni biyu da suka gabata mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya kori gwamna David Umahi na jihar Ebonyi da mataimakinsa Kelechi Igwe da kuma wasu ‘yan majalisar dokokin jihar su 15 da suka sauya sheka daga PDP zuwa APC.
A ranar Litinin din da ta gabata ne, mai shari’a Taiwo Taiwo na wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ya kori ‘yan majalisar dokokin jihar Cross River su 20 saboda sauya sheka daga PDP zuwa APC.