Lamarin ya faru ne a jihar Kaduna, yayin da wata bazawara ta ce za ta koma gidan tsohon mijinta a na saura kwana 10 da aurenta da wani saurayi.
Saurayin ya maka ta a kotun majistare, inda ya ce, ta karbi kudi akalla milyan goma a hannunsa.
Alkalin kotu ya bada belinta tare da kafa mata wasu sharruda masu tsauri.
Fatima Sanusi, ta gurfana gaban kotu kan zargin ta damfari saurayin da a ka sanya musu rana, kuma ta ce ta fasa a na sauran kwanaki 10 da auren ta.
An gurfanar da Fatima Sanusi ne a kotun Majistare dake unguwar Barnawa a jihar Kaduna.
Daily Trust ta rawaito cewa, an shirya komai domin auren su, amma Fatima ta ce ta fasa auren Umar Oruma a na saura kwanaki goma a shafa Fatiha, yanzu ta na son komawa wajen tsohon mijinta.