fidelitybank

Saura kiris a kammal kasuwar Gwal a Kano – Ministan Ma’adanai

Date:

Ministan ma’adinai da karafa, Olamilekan Adegbite, ya tabbatar da cewa, za a kammala aikin kasuwar Zinariya wato Gwal a jihar Kano kafin karshen shekarar 2022.

Ministan y a bayyana haka ne a ranar Talata a Kano a lokacin da yake duba aikin ginin katafaren kasuwar ta zinare.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai mai taken gwamnatin tarayya domin kammala Kano Gold Souk a bana da ma’aikatar ta fitar a ranar Laraba.

Sanarwar ta kara da cewa, “Gwamnatin Buhari ta ba da tabbacin cewa, za ta kammala aikin kasuwar Gwal a Kano kafin karshen shekarar 2022.”

Ya ci gaba da cewa, “Samar da kasuwar a Kano na daga cikin kokarin gwamnati mai ci na samar da dabarun kere-kere na fasaha da kananan ma’adanai a kowane shiyyoyi shida na siyasar kasar nan, domin yin amfani da damar masu sana’a da masu hakar ma’adinai. masu aiki a kasar.”

Ministan ya na cewa, “Muna so a kara habaka gwal dinmu a Najeriya, domin mu kara daraja, mu samar da ayyukan yi ga jama’armu tare da samar da kudaden shiga ga gwamnati,” in ji shi.

An gina katafaren kasuwar ta Zinare ne a karamar hukumar Kumbotso da ke Jihar Kano, kuma a na ci gaba da aikin na tsawon watanni hudu.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp