Ministan ma’adinai da karafa, Olamilekan Adegbite, ya tabbatar da cewa, za a kammala aikin kasuwar Zinariya wato Gwal a jihar Kano kafin karshen shekarar 2022.
Ministan y a bayyana haka ne a ranar Talata a Kano a lokacin da yake duba aikin ginin katafaren kasuwar ta zinare.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai mai taken gwamnatin tarayya domin kammala Kano Gold Souk a bana da ma’aikatar ta fitar a ranar Laraba.
Sanarwar ta kara da cewa, “Gwamnatin Buhari ta ba da tabbacin cewa, za ta kammala aikin kasuwar Gwal a Kano kafin karshen shekarar 2022.”
Ya ci gaba da cewa, “Samar da kasuwar a Kano na daga cikin kokarin gwamnati mai ci na samar da dabarun kere-kere na fasaha da kananan ma’adanai a kowane shiyyoyi shida na siyasar kasar nan, domin yin amfani da damar masu sana’a da masu hakar ma’adinai. masu aiki a kasar.”
Ministan ya na cewa, “Muna so a kara habaka gwal dinmu a Najeriya, domin mu kara daraja, mu samar da ayyukan yi ga jama’armu tare da samar da kudaden shiga ga gwamnati,” in ji shi.
An gina katafaren kasuwar ta Zinare ne a karamar hukumar Kumbotso da ke Jihar Kano, kuma a na ci gaba da aikin na tsawon watanni hudu.