Ma’aikatar Tsaro ta Birtaniya ta ce, dandazo dakarun Rasha na gab da shiga Kyiv babban birnin Ukraine, inda ya rage musu kilomita 25 kacal.
A cikin bayanan da ta saba fitarwa, Birtaniya ta ce, bataliyar da ke Arewacin birnin ya rarrabu, kuma babu mamaki, domin su taimaka wajen zagaye birnin.
Ta ce, “Babu mamaki kuma Rasha ta yi haka ne, domin ta rage haÉ—arin kai wa sojojinta hari daga dakarun Ukraine, waÉ—anda har yanzu suke Æ™ara nuna turjiya,” a cewar ma’aikatar.
A gefe guda kuma, garuruwan Chernihiv, da Kharkiv, da Mariupol a zagaye suke, sannan kuma suna ci gaba da fuskantar luguden wuta daga dakarun Rasha. In ji BBC.