An zaɓi ƙasar Saudiyya a matsayin ƙasar da za ta karɓi baƙuncin gasar kofin duniya ta ƙungiyoyi a karon farko.
An bayyana matakin ne kwana uku bayan da Real Madrid ta ɗauki kofin a Morocco, bayan da ta casa Al- Hilal da ci 5-3, ƙungiyar Saudiyya ta farko da ta kai wasan ƙarshe a gasar.
Saudiyya da za ta kasance ƙasa ta shida da ta ɗauki baƙuncin gasar tun bayan ɓullo da ita a shekarar 2000.
Ministan wasanni na ƙasar ya ce ɗaukar nauyin gasar alama ce da ke nuna cewa ”karanmu ya kai tsaiko”.
A ‘yan shekarun baya-bayan nan dai ƙasar Saudiyya na ta zuba jari a ɓangaren wasanni, lamarin da ya sa wasu ke zarginta da zubar da martabar ƙasar.
Haka kuma ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam ciki har da Amnesty International na zargin ƙasar da take haƙƙin bil adama.