Rahotanni daga Saudiyya na bayyana cewa hukumomi sun zartas da hukuncin kisa kan wasu ƴan ƙasar guda huɗu a cikin kwanaki biyu da suka gabata, bayan samun su da laifukan ta’addanci.
Hakan ya kawo waɗanda aka zartaswa hukuncin kisa a ƙasar zuwa mutum bakwai a wannan watan, waɗanda yawanci suka fito daga yankunan da ƴan Shi’a suka fi rinjaye.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar ta ruwaito ma’aikatar harkokin cikin gida na cewa cikin laifukan da aka samu mutanen, sun haɗa da leƙen asiri da kafa kungiyoyin ta’addanci da far wa jami’an tsaro da kuma koyon sarrafa maƙamai da amfani da bama-bamai.
Hukumomin Saudiyya sun zartas da hukuncin kisa kan mutum 36 tun soma wannan shekara, idan aka kwatanta da 147 na bara, a cewar bayanai da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu.
Kungiyoyin kare hakkin ɗan adam sun sha sukar masarautar ta Saudiyya kan ƙaruwar mutanen da take zartas wa hukuncin kisa