A ranar Juma’ar da ta gabata ne kungiyar agaji ta Islamic Relief Organisation (IIRO) ta kasar Saudiyya ta raba alawus na naira miliyan 131 ga marayu 1,960 a jihar Kebbi.
Da yake kaddamar da tallafin a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar, Gwamna Atiku Bagudu, ya nuna jin dadinsa ga IIRO, bisa wannan karimcin da ya yi, ya kuma yi kira da a ci gaba da gudanar da shirin.
Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa, NAN, ya ruwaito cewa, an raba kudaden ne ta hannun kungiyar Islamic League, ofishin Kaduna.
Gwamnan wanda ya samu wakilcin Alhaji Babale Umar-Yauri, sakataren gwamnatin jihar (SSG), ya bada tabbacin cewa, gwamnati mai ci a jihar ta sanya kari akan duk wani abu da ya shafi marayu.