fidelitybank

Saudiyya ta dakatar da duk wani mai niyar shiga kasar ta sai masu aikin Hajji kawai

Date:

Ƙasar Saudiyya ta ce daga ranar 29 ga watan Afrilun da muke ciki ba wanda za ta bari ya shiga ƙasar sai mai ɗauke da bizar aikin hajji.

Jaridar Saudi Gazzet ta ambato ma’aikatar cikin gida ta ƙasar na bayyana haka cikin sabbin matakan da ta ɗauka kan tsare-tsaren aikin hajjin bana.

Sabbin matakan sun tanadi cewa za a haramta wa ƴan asalin ƙasar mazauna ƙetare shiga birnin Makka, in ba da wani muhimmin dalili ba.

Ma’aikatar ta ƙara da cewa za a bai wa asalin ƴan ƙasar izinin shiga birnin Makka ne kawai idan adireshin gidansu ya nuna cewa a birnin suke da zama, ko waɗanda aka bai wa damar yin aiki a harami.

A cewar ma’aikatar harkokin cikin gidan wannan wani mataki ne manyan sauye-sauye da ta ɓullo da su domin lura da aikin hajjin bana na tabbatar da lafiya da tsaron mahajjata.

Ma’aikatar ta ƙara da cewa daga ranar 13 ga watan Afrilu, ƙasar za ta daina bayar da biza ga masu zuwa ibadar Umara, yayin da ta saka ranar 29 ga watan Afrilun a matsayin ranar da masu ziyarar Umara daga ƙasashen waje za su fice daga ƙasar, domin bayar da damar shirye-shiryen aikin hajji.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp