Ƙasar Saudiyya ta ce daga ranar 29 ga watan Afrilun da muke ciki ba wanda za ta bari ya shiga ƙasar sai mai ɗauke da bizar aikin hajji.
Jaridar Saudi Gazzet ta ambato ma’aikatar cikin gida ta ƙasar na bayyana haka cikin sabbin matakan da ta ɗauka kan tsare-tsaren aikin hajjin bana.
Sabbin matakan sun tanadi cewa za a haramta wa ƴan asalin ƙasar mazauna ƙetare shiga birnin Makka, in ba da wani muhimmin dalili ba.
Ma’aikatar ta ƙara da cewa za a bai wa asalin ƴan ƙasar izinin shiga birnin Makka ne kawai idan adireshin gidansu ya nuna cewa a birnin suke da zama, ko waɗanda aka bai wa damar yin aiki a harami.
A cewar ma’aikatar harkokin cikin gidan wannan wani mataki ne manyan sauye-sauye da ta ɓullo da su domin lura da aikin hajjin bana na tabbatar da lafiya da tsaron mahajjata.
Ma’aikatar ta ƙara da cewa daga ranar 13 ga watan Afrilu, ƙasar za ta daina bayar da biza ga masu zuwa ibadar Umara, yayin da ta saka ranar 29 ga watan Afrilun a matsayin ranar da masu ziyarar Umara daga ƙasashen waje za su fice daga ƙasar, domin bayar da damar shirye-shiryen aikin hajji.