fidelitybank

Saudiyya ta aiwatar da hukuncin kisa ga mutane 81

Date:

Saudiyya ta sanar da cewa ta ƙaddamar da hukuncin kisa a kan mutum 81 da kotu ta yanke wa hukunci kan laifuka da suka shafi ta’addanci da fyaɗe da kisa, kamar yadda kamfanin labarai na ƙasar SPA ya ruwaito.

Wata sanarwa daga ma’aikatar harkokin cikin gida ta ce daga cikin mutanen akwai mambobin ƙungiyar ISIS da Al-Qaeda da Houthi.

“Mutanen da suka kai 81, an yanke musu hukunci ne kan laifuka daban-daban, ciki har da kashe mutane maza da mata da yara ƙanana,” in ji sanawar.

“Laifukan sun haɗa da shiga ƙungiyoyin ta’adddanci na ƙasashen waje kamar ISIS da Al-Qaeda da Huothi da ke kai hare-hare a cikin ƙasa (Saudiyya) da kuma zuwa wuraren rikici don taya ƙungiyoyin ta’addanci yaƙi.”

Ta ƙara da cewa an kama mutanen ne sannan aka yi musu shari’a a Saudiyya ƙarƙashin jagorancin alƙalai 13 a mataki uku daban-daban na shari’a kan kowane ɗayansu. In ji BBC.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp