fidelitybank

Saudiyya ta aiwatar da hukuncin kisa ga mutane 81

Date:

Saudiyya ta sanar da cewa ta ƙaddamar da hukuncin kisa a kan mutum 81 da kotu ta yanke wa hukunci kan laifuka da suka shafi ta’addanci da fyaɗe da kisa, kamar yadda kamfanin labarai na ƙasar SPA ya ruwaito.

Wata sanarwa daga ma’aikatar harkokin cikin gida ta ce daga cikin mutanen akwai mambobin ƙungiyar ISIS da Al-Qaeda da Houthi.

“Mutanen da suka kai 81, an yanke musu hukunci ne kan laifuka daban-daban, ciki har da kashe mutane maza da mata da yara ƙanana,” in ji sanawar.

“Laifukan sun haɗa da shiga ƙungiyoyin ta’adddanci na ƙasashen waje kamar ISIS da Al-Qaeda da Huothi da ke kai hare-hare a cikin ƙasa (Saudiyya) da kuma zuwa wuraren rikici don taya ƙungiyoyin ta’addanci yaƙi.”

Ta ƙara da cewa an kama mutanen ne sannan aka yi musu shari’a a Saudiyya ƙarƙashin jagorancin alƙalai 13 a mataki uku daban-daban na shari’a kan kowane ɗayansu. In ji BBC.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp