Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa, ya tsaya takarar gwamna har sau hudu kafin daga bisani ya samu nasara a shekarar 1999.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin da yake tattaunawa da shugabannin kungiyoyin tallafi sama da 200 a fadin kasar nan a Abuja.
Da yake jawabi ga shugabannin kungiyoyin, Atiku, ya ce, ya ji dadin yadda matasa ke shiga harkokin siyasa a yau, inda ya ce, burinsa shi ne ya jagoranci matasa ya mika musu tsarin siyasarsa.
Ya kuma bukaci matasa da su kasance masu tsayin daka tare da jajircewa wajen cimma burinsu.
“Abin farin ciki ne a kwanakin nan na ga matasa da yawa sun zo wurina suna bayyana kudirinsu na tsayawa takara a mukamai daban-daban na siyasa, wasu majalisun jihohi, wasu majalisun kasa har ma da wasu na neman zama gwamna.