Yayin da al’ummar Musulmi ke gudanar da bukukuwan karamar Sallah na shekarar 2022, Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su so juna su zabi shugabanni masu nagarta a zabuka masu zuwa, tare da nuna matukar damuwa game da hauhawar farashin kayan abinci da kayan masarufi a kasar.
A cikin sakonsa na Sallah, Sarkin Musulmi, ya bukaci al’ummar Musulmi da su yi addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar. A cikin sakon da Daraktan Gudanarwa, NSCIA, Arc. Zubairu Haruna Usman-Ugwu, Sarkin Musulmi ya roki gwamnati da ta kawo karshen hauhawar farashin kayayyaki, yayin da ya bukaci ‘yan kasuwa da su daina kara farashin kayan abinci ba gaira ba dalili.
Ya kuma yi kira ga ’yan siyasa da su dauki siyasa a matsayin hidima ga kasa, wanda bai kamata a yi ta a matsayin abin yi ko a mutu ba.