Daya daga cikin manyan sarakunan Najeriya, Maigari na Lokoja, Alhaji (Dr) Muhammad Kabir Maikarfi lll ya rasu.
Maigari mai shekaru 80 ya rasu da yammacin Laraba bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa da ke Abuja.
Ya kasance daya daga cikin sarakunan gargajiya mafi dadewa a jihar Kogi, inda ya hau karagar mulki a shekarar 1992.
Sakataren Majalisar Gargajiya na karamar hukumar Lokoja, Muhammed Nalado Usman ya tabbatar da rasuwar basaraken a wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba.
Sanarwar ta ce za a yi jana’izar mahaifin marigayin a ranar Alhamis a Lokoja da karfe 4 na yamma.