Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a harkar yawon bude ido da su wayar da kan jama’a game da sha’anin yawon bude ido a cikin gida da kuma kara himma a harkokin sufurin jiragen sama zuwa Kano.
Sarkin, wanda ya yi wannan kiran a taron masu ruwa da tsaki na yankin Arewa-maso-Yamma da aka gudanar a Kano, ya kuma yabawa hukumar bunkasa yawon bude ido ta Najeriya, kan inganta harkar yawon bude ido a kasar nan.
A nasa jawabin, babban daraktan hukumar bunkasa yawon bude ido ta Najeriya, Cif Folorunsho Coker, ya bayyana cewa, yadda masana’antar yawon bude ido ta Najeriya ta yi na’urar tantancewa ya sa aka samu saukin harkokin yawon bude ido a Najeriya.