fidelitybank

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Date:

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero ya soke duk wasu shirye-shiryen gudanar da sallar Idi na bana, saboda dalilan tsaro.

Hakan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren masarautar, Malam Awaisu Abbas Sanusi wanda ya kara da cewa an cimma matsayar ne bayan tuntubar juna.

Ya ce Masarautar ta tattauna da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki, inda suka bayar da misali da yiwuwar tabarbarewar tsaro daga wasu marasa gaskiya.

Awaisu ya kara da cewa matakin dakatar da duk wani shiri na durbar shine don kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Ba wannan ne karon farko da aka yanke irin wannan hukunci ba.

An kuma aiwatar da irin wannan dakatarwar a lokacin bikin Eid-el-Fitr da ya gabata a farkon wannan shekarar, inda kuma aka dakatar da jerin gwano saboda irin wadannan dalilai.

Masarautar ta bukaci mazauna yankin da su ci gaba da yin addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a Kano da ma Najeriya baki daya.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da jihar Kano ta amince da masarautu, karkashin jagorancin Khalifa Muhammadu Sanusi II ya fara shirye-shiryen gudanar da bukukuwan Sallah duk da gargadin da ‘yan sanda suka yi.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp