Matashiyar da ta lashe gasar kyau na Najeriya, Shatu Garko, ta magantu a kan gwagwarmayar da ta sha a farkon tafiyarta a matsayin ta na mai sanya hijabi.
Garko mai shekaru 18 a duniya, wacce ta lashe gasar na 44, inda ta lallasa abokan takara 18 wajen zama sarauniyar kyau mai hijabi ta farko ta bayyana hakan ne a wata hira da jaridar The Punch.
Ta bayyana cewa, da farko ta ji tsoro saboda hijabinta. A cewarta, kamfanoni da dama sun ki aiki da ita, saboda hakan inda ta ce, suna bata shawarar da ta cire hijabin idan ta na so ta yi nasara a harkar tallace-tallace.
Ta ce: “Na fara tallata kayan ado ne tsawon kasa da shekara daya. Bayan na kammala makaranta, ina garkame a gida, saboda annobar korona. Na tsani zama haka babu aikin yi, sai na yanke shawarar gwada tallata kaya. Aikin farko da na yi ya kasance da tangarda. Da farko sun dauke ni, amma sai daga baya suka ce ina bukatar jagoranci mai inganci, sannan suka yi watsi da ni”. A cewar Shatu.