Ministan Harkokin Waje na Turkiyya Mevlut Cavusoglu da ke shiga tsakani a tattaunawar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine, ya ce an samu ci gaba tsakanin ɓangarorin biyu.
Cavusoglu ya faɗa wa kamfanin labarai na AFP cewa “ba abu ne mai sauƙi ba a cimma a matsaya yayin da ake ci gaba da fafata yaƙi, yayin da ake kashe fararen hula”, amma ya ƙara da cewa “mun ga alamun suna ƙoƙarin cimma yarjejeniya”.
Ministan ya ziyarci Rasha da Ukraine a makon nan sakamakon ƙawancen da Turkiyya ke yi da ƙasashen biyu. In ji BBC.
Ya ce Turkiyya na tuntuɓar tawagogin da ke tattaunawa da juna amma ya ƙi bayyana abin da tattaunawar ta ƙunsa saboda “Turkiyya na taka rawar mai sasanci ta gaskiya”.
Ɓangarorin biyu na yunƙurin cimma yarjejeniya a kan abu shida:
- Ukraine ta zama ‘yar ba-ruwana
- Ukraine za ta watsar da makamanta
- Abin da Rasha ta kira “kakkaɓe ‘yan ta’adda daga Ukraine”
- Cire duk wani tsari da zai hana amfani da harshen Rashanci a Ukraine
- Matsayin yankuna biyu da suka ɓalle daga Ukraine na Donbass
- Matsayin yankin Crimea da Rasha ta ƙwace a 2014
Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya faɗa cikin wani bidiyo ranar Asabar cewa: “Wannan ne lokacin da ya kamata a haɗu, a tattauna, lokaci ne da za a fayyace iyakoki da kuma yi wa Ukraine adalci.”