fidelitybank

Sarau kiris a cimma yarjejeniya tsakanin Rasha da Ukraine

Date:

Ministan Harkokin Waje na Turkiyya Mevlut Cavusoglu da ke shiga tsakani a tattaunawar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine, ya ce an samu ci gaba tsakanin ɓangarorin biyu.

Cavusoglu ya faɗa wa kamfanin labarai na AFP cewa “ba abu ne mai sauƙi ba a cimma a matsaya yayin da ake ci gaba da fafata yaƙi, yayin da ake kashe fararen hula”, amma ya ƙara da cewa “mun ga alamun suna ƙoƙarin cimma yarjejeniya”.

Ministan ya ziyarci Rasha da Ukraine a makon nan sakamakon ƙawancen da Turkiyya ke yi da ƙasashen biyu. In ji BBC.

Ya ce Turkiyya na tuntuɓar tawagogin da ke tattaunawa da juna amma ya ƙi bayyana abin da tattaunawar ta ƙunsa saboda “Turkiyya na taka rawar mai sasanci ta gaskiya”.

Ɓangarorin biyu na yunƙurin cimma yarjejeniya a kan abu shida:

  • Ukraine ta zama ‘yar ba-ruwana
  • Ukraine za ta watsar da makamanta
  • Abin da Rasha ta kira “kakkaɓe ‘yan ta’adda daga Ukraine”
  • Cire duk wani tsari da zai hana amfani da harshen Rashanci a Ukraine
  • Matsayin yankuna biyu da suka ɓalle daga Ukraine na Donbass
  • Matsayin yankin Crimea da Rasha ta ƙwace a 2014

Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya faɗa cikin wani bidiyo ranar Asabar cewa: “Wannan ne lokacin da ya kamata a haɗu, a tattauna, lokaci ne da za a fayyace iyakoki da kuma yi wa Ukraine adalci.” 

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp