fidelitybank

Sarakunan gargajiya ba sa tsoron Gwamnoni – Sarkin Musulmi

Date:

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Sa’ad Mohammad Abubakar II, ya musanta maganar da ake yi cewa sarakunan gargajiya suna tsoron gwamnoni.

Sarkin musulmin ya ce sarakunan gargajiya sun kasance jagorori a ƙasar tun kafin ta samu ƴancin kai, sannan ya ƙara da cewa sarakunan sun fi gwamnonin fahimtar yanayin ƙasar.

Ya bayyana hakan ne a wani taro na ƙungiyar ci gaban matasan arewacin Najeriya da Gidauniyar Tunawa da Sardauna ta shirya a Abuja a ranar Talata kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Tun da farko, tsohon gwamnan jihar Neja, Babangida Aliyu, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya suna tsoron gwamnoni.

Da yake mayar da martani, sarkin na Musulmi ya ce, “Na ji an ce sarakunan gargajiya na tsoron gwamnoninsu. Ba haka ba ne, sarakuna ba sa tsoron gwamnoni. Sarakunan gargajiya suna girmama kansu ne, sannan suna girmamma gwamnonin domin suna da iko a jihohinsu.

“Duk lokacin da wani abu ya faru, muna mayar da shi zuwa ga Allah ne. Muna kawo sauyi, kuma muna karɓar sauyi a yadda suka zo mana. Duk mun sani, akwai sarakunan gargajiya a Najeriya tun a shekarar 1824, amma a shekarar 1960 ce Najeriya ta samu ƴanci.”

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp