Mai alfarma Sarkin Musulmi, Sa’ad Mohammad Abubakar II, ya musanta maganar da ake yi cewa sarakunan gargajiya suna tsoron gwamnoni.
Sarkin musulmin ya ce sarakunan gargajiya sun kasance jagorori a ƙasar tun kafin ta samu ƴancin kai, sannan ya ƙara da cewa sarakunan sun fi gwamnonin fahimtar yanayin ƙasar.
Ya bayyana hakan ne a wani taro na ƙungiyar ci gaban matasan arewacin Najeriya da Gidauniyar Tunawa da Sardauna ta shirya a Abuja a ranar Talata kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Tun da farko, tsohon gwamnan jihar Neja, Babangida Aliyu, ya bayyana cewa sarakunan gargajiya suna tsoron gwamnoni.
Da yake mayar da martani, sarkin na Musulmi ya ce, “Na ji an ce sarakunan gargajiya na tsoron gwamnoninsu. Ba haka ba ne, sarakuna ba sa tsoron gwamnoni. Sarakunan gargajiya suna girmama kansu ne, sannan suna girmamma gwamnonin domin suna da iko a jihohinsu.
“Duk lokacin da wani abu ya faru, muna mayar da shi zuwa ga Allah ne. Muna kawo sauyi, kuma muna karɓar sauyi a yadda suka zo mana. Duk mun sani, akwai sarakunan gargajiya a Najeriya tun a shekarar 1824, amma a shekarar 1960 ce Najeriya ta samu ƴanci.”