Gwamnatin jihar Edo a ranar Laraba, 18 ga watan Janairu, ta tabbatar da kame wasu sarakunan kauye biyu dangane da harin jirgin kasa na ranar Asabar, 7 ga watan Janairu wanda yayi sanadiyar yin garkuwa da fasinjoji 20 a tashar jirgin kasa ta Igueben.
Kwamishinan sadarwa da wayar da kan jama’a na jihar, Chris Nehikhare, ya kara da cewa an kama wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a lamarin.
Nehikhare ya kara da cewa sauran fasinjoji biyun da aka yi garkuwa da su, jami’an tsaro kuma sun ceto su.
A halin da ake ciki kuma, babban sufeton ‘yan sandan ya tura wata tawaga ta musamman domin ceto wadanda harin jirgin kasa ya rutsa da su a Edo.
Rahotanni sun ce akalla fasinjoji 31 ne aka yi garkuwa da wasu da ake zargin Fulani makiyaya ne. A halin da ake ciki, an kuma tattaro wasu manyan jami’an gwamnati suma na cikin fasinjojin.