fidelitybank

Sarakuna da Hakimai su fara shirye-shiryen hawan Sallah – Gwamnan Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umarci dukkanin masarautun jihar guda hudu da su fara shirye-shiryen bikin Sallah.

Ya ba wa ‘yan kasa da maziyarta tabbacin gudanar da bukukuwan da ba a mantawa da su ba.

Sanarwar ta fito ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, bayan wani taron buda baki da suka yi da sarakunan gargajiya a fadar gwamnati da ke Kano.

A cewar sanarwar, gwamna Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kiyaye dimbin al’adun gargajiya na Kano, inda ya bayyana cewa Durbar al’ada ce mai matukar kima a tsakanin al’ummar jihar.

“Mutanen Kano na hakin bikin Sallah Durbar, inda suke sanye da sabbin kaya, su taru a kan tituna suna kallon sarakunan su a doki, kuma ba za mu bari wani abokin gaba ya hana ‘yan kasa wannan hakki ba.

Domin tabbatar da tsaron lafiyar mahalarta taron da ’yan kallo, Gwamna Yusuf ya bayyana cewa, dukkanin hukumomin tsaro a jihar za su ba da himma wajen tabbatar da ingantaccen tsaro a duk lokacin bukukuwan.

Ya kara da cewa, “Muna aiki kafada da kafada da jami’an tsaro don tabbatar da cewa kowa zai iya shiga Durbar ba tare da tsoro ba.

Gwamna Yusuf ya kuma bayyana shirin kaddamar da masarautar Kano a hukumance a watan Afrilu, inda ya jaddada rawar da take takawa wajen karfafa harkokin mulki da al’adu.

Gwamna Yusuf ya kuma yabawa sarakunan kan yadda suka kulla alaka mai kyau tun lokacin da aka nada su, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da ba a taba ganin irinsa ba a tsakanin sarakunan jihar.

Ya kuma bayyana fatansa cewa, hadin gwiwa tsakanin gwamnati da masarautu zai kara inganta al’adun Sallah Durbar da kuma samar da zaman lafiya a jihar.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp