Dubban matasa a jihar Kwara, sun yi gangami a Ilorin, domin nuna goyon bayansu ga Bukola Saraki ya tsaya takara a 2023.
Matasan sun bayyana cewa, Saraki ne ya fi cancanta ya zama shugaban kasa duba da cewar yankin Arewa ta tsakiya bai taba shugabanci ba a kasar nan.
Sun kuma ce tsohon shugaban majalisar dattawan zai hada kan kasar tare da bunkasa tattalin arzikinta
Jaridar Punch ta rawaito cewa, matasan karkashin inuwar kungiyar Grow Nigeria Youth Movement, sun hadu a filin wasa na jihar Kwara tun da misalin karfe 7:00 na safe, inda suka zagaya yankunan Taiwo, Unity, Challenge da Post Office, kafin su tsaya a gidan tsohon shugaban majalisar dattawan da ke GRA.
Da yake jawabi a taron a madadin Saraki, shugaban jam’iyyar PDP kuma tsohon kakakin majalisar jihar, Babatunde Mohammed, ya ce, abun da matasan suka yi ya yi daidai da kiraye-kirayen da ake yi kan yankin Arewa maso tsakiya ya samar da shugaban kasa kuma a hadu a kan Saraki.