fidelitybank

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Date:

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu fararen hula 35 a ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda a jihar Zamfara.

Cikin wani saƙon jaje da ƙungiyar ta aike ranar Laraba a Abuja, shugaban ƙungiyar Sanata Abdulaziz Yar’adua,ya jajanta wa al’ummar yankin musamman iyalan waɗanda lamarin ya shafa.

A farkon makon nan ne ƴanbindiga suka yi wa su mutanen yankan rago duk kuwa da biyan kuɗin fansa da aka ce iyalansu sun yi domin kuɓutar da su.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin Najeriya da ke fama da ayyukan ƴanbindiga masu sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Wasu masu sharhi dai na ci gaba da sukar gwamnati da masu ruwa da tsaki a harkar tsaron ƙasar kan rashin samar da zaman lafiya a yankin.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp