Sanatoci 109 na Tarayyar Najeriya sun bayar da gudunmawar albashin watan Disamba ga wadanda harin bam da ya rutsa da su a Kaduna a ranar Lahadin da ta gabata.
Kamar yadda Aminiya ta ruwaito, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin ne ya sanar da hakan a ranar Lahadin da ta gabata a gidan gwamnatin Jihar Kaduna a lokacin da ya jagoranci wata babbar tawaga ta ‘yan majalisar dattijai zuwa jihar.
Gwamna Uba Sani ne ya tarbi Sanatocin a gidan gwamnati.