Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar mazaɓar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawan Najeriya ta shigar da shugaban majalisar ƙara a gaban kotu kan ɓata mata suna.
A ƙarar da ta shigar gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja ranar Talata, ‘yarmajalisar ta zargi Sanata Godswill Akpabio da mataimakinsa na musamman, Mfon Patrick, da yin kalaman ɓata suna a kanta.
Ta nemi kotun ta tilasta wa mutanen janye kalaman, su nemi afuwarta a wani shafin jarida, sannan su biya ta diyyar naira biliyan 100.
Ta ɗora zargin nata ne kan wani saƙo da ta ce Mista Patrick ya wallafa a shafinsa na dandalin Facebook, inda ya soke ta cewa “ba ta san komai ba game da zaman majalisa…da kuma saka tufafi masu shara-shara”.
A makon da ya gabata ne sanatar da shugaban suka yi cacar baki a zauren majalaisar bayan Akpabio ya sauya mata wurin zama, abin da ya jawo cecekuce tsakanin ‘yan Najeriya musamman a shafukan sada zumunta.