fidelitybank

Sanata Shehu Sani ya mayarwa da Sarkin Kano martani a kan Mata su rama duka

Date:

Tsohon Senatan da ya wakilci Yankin Kaduna Tsakiya, Shehu Sani, ya soki kalaman da Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, yayi game da mayarda martani a aure.

A tuna cewa Sanusi ya ba ‘ya’yansa shawara da su mayar da martani idan mazajensu sun buge su, wani magana da yayi a lokacin taron Tattaunawar Kasa kan cin zarafin Jinsi (GBV) a Jami’ar Bayero, Kano

A cikin martani da yayi a shafinsa na Facebook, Sani ya bayyana kin amincewa da tallata kawo ramuwar gayya ta hanyar tashin hankali, yana mai jaddada cewa hakan na iya lalata aure.

“Mai Martaba Sanusi bai kamata ya karfafa irin wannan ba, ta hanyar bugu da mayar da martani. Maimakon haka, maza da mata su koyi yadda za su kula da kansu a lokacin fushin,” ya rubuta.

Tsohon senatan ya bayyana cewa warware rikice-rikice cikin lumana shi ne mafita mai ɗorewa.

“Idan mijin yana fushi, ya kamata ya fita daga gidan sannan ya dawo daga baya. Idan mijin yana jin haushi yana ihu, matar tayi shuru kawai ta bar shi ya fitar da dukkan maganganunsa.”

“Kalmar ‘A yi haƙuri’ tana da ƙarfi a cikin gida,” ya kara da cewa.

Ya yi gargadi cewa, “Ranar da buga juna da mayar da martani ya zama al’ada a cikin gida, aure zai lalace ba tare da wani gyara ba, ko da kuwa ma’auratan suna ci gaba da zama tare.”

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp