fidelitybank

Sanata Shehu Sani ya mayarwa da Sarkin Kano martani a kan Mata su rama duka

Date:

Tsohon Senatan da ya wakilci Yankin Kaduna Tsakiya, Shehu Sani, ya soki kalaman da Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, yayi game da mayarda martani a aure.

A tuna cewa Sanusi ya ba ‘ya’yansa shawara da su mayar da martani idan mazajensu sun buge su, wani magana da yayi a lokacin taron Tattaunawar Kasa kan cin zarafin Jinsi (GBV) a Jami’ar Bayero, Kano

A cikin martani da yayi a shafinsa na Facebook, Sani ya bayyana kin amincewa da tallata kawo ramuwar gayya ta hanyar tashin hankali, yana mai jaddada cewa hakan na iya lalata aure.

“Mai Martaba Sanusi bai kamata ya karfafa irin wannan ba, ta hanyar bugu da mayar da martani. Maimakon haka, maza da mata su koyi yadda za su kula da kansu a lokacin fushin,” ya rubuta.

Tsohon senatan ya bayyana cewa warware rikice-rikice cikin lumana shi ne mafita mai ɗorewa.

“Idan mijin yana fushi, ya kamata ya fita daga gidan sannan ya dawo daga baya. Idan mijin yana jin haushi yana ihu, matar tayi shuru kawai ta bar shi ya fitar da dukkan maganganunsa.”

“Kalmar ‘A yi haƙuri’ tana da ƙarfi a cikin gida,” ya kara da cewa.

Ya yi gargadi cewa, “Ranar da buga juna da mayar da martani ya zama al’ada a cikin gida, aure zai lalace ba tare da wani gyara ba, ko da kuwa ma’auratan suna ci gaba da zama tare.”

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp