fidelitybank

Sanata Mace ta farko a Najeriya ta rasu

Date:

Mace ta farko a Najeriya da ta fara zama Sanata, Gimbiya Franca Afegbua, ta rasu ta na da shekaru 81 a duniya.

Franca Afegbua wadda aka haifa a shekarar 1942, ta rasu ne da sanyin safiyar Lahadi a daya daga cikin asibitoci masu zaman kansu a birnin Benin.

Kassim Afegbua, daya daga cikin kannenta, dan jaridan da ya taba rike mukamin kwamishinan yada labarai a gwamnatin Adams Oshiomhole a jihar Edo, kuma a halin yanzu mamba ne a kungiyar yakin neman zaben Tinubu, ya tabbatar wa wakilin Daily Idependent.

Kassim ya ce ‘yar uwarta ta rasu ne da safiyar Lahadi kuma an kai gawar ta zuwa dakin ajiye gawa na UBTH.

Karanta Wannan: Tinubu zai gana da zababbun ‘yan majalisa

Sanata Gimbiya Franca Afegbua da aka zaba a kan turbar rusasshiyar jam’iyyar National Party of Nigeria (NPN) a shekarar 1983, ta wakilci gundumar Bendel ta Arewa a tsohuwar jihar Bendel.

Ta yi aiki a babban zauren majalisar tarayya daga Oktoba zuwa Disamba 1983 kafin juyin mulkin soja na Buhari ya kawo karshen jamhuriya ta biyu a ranar 31 ga Disamba, 1983.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp