Mace ta farko a Najeriya da ta fara zama Sanata, Gimbiya Franca Afegbua, ta rasu ta na da shekaru 81 a duniya.
Franca Afegbua wadda aka haifa a shekarar 1942, ta rasu ne da sanyin safiyar Lahadi a daya daga cikin asibitoci masu zaman kansu a birnin Benin.
Kassim Afegbua, daya daga cikin kannenta, dan jaridan da ya taba rike mukamin kwamishinan yada labarai a gwamnatin Adams Oshiomhole a jihar Edo, kuma a halin yanzu mamba ne a kungiyar yakin neman zaben Tinubu, ya tabbatar wa wakilin Daily Idependent.
Kassim ya ce ‘yar uwarta ta rasu ne da safiyar Lahadi kuma an kai gawar ta zuwa dakin ajiye gawa na UBTH.
Karanta Wannan:Â Tinubu zai gana da zababbun ‘yan majalisa
Sanata Gimbiya Franca Afegbua da aka zaba a kan turbar rusasshiyar jam’iyyar National Party of Nigeria (NPN) a shekarar 1983, ta wakilci gundumar Bendel ta Arewa a tsohuwar jihar Bendel.
Ta yi aiki a babban zauren majalisar tarayya daga Oktoba zuwa Disamba 1983 kafin juyin mulkin soja na Buhari ya kawo karshen jamhuriya ta biyu a ranar 31 ga Disamba, 1983.