fidelitybank

Sanata Barau ya dauki nauyin Matasa 70 su karo karatu a kasar Indiya

Date:

Sanata Barau Jibrin, mai wakiltar Kano ta Arewa, ya ɗauki nauyin matasa 70 daga jihar Kano don yin karatun digiri na biyu a kasar India.

Wannan shiri na tallafin karatu ya mayar da hankali ne kan bangarorin kimiyya da fasaha, musamman Fasahar zamani (Artificial Intelligence), Kimiyyar Mutumi-mutumi (Robotics), da sauran fannoni na zamani.

Da yake magana a lokacin da yake raka matasan zuwa filin jirgin sama, Sanata Barau ya bayyana cewa manufar wannan shiri shi ne tallafa wa matasa daga gidajen talakawa domin samun ilimin da zai taimakesu da al’ummar baki ɗaya.

“Mun san cewa babban kalubalen Arewa shine rashin ilimi. Yawan matasa albarka ne, amma wannan albarka ba za ta amfani kasa ba sai an basu ilimi mai inganci. Saboda haka, na ɗauki nauyin tura matasa 70 zuwa India domin samun ilimin da zai canza rayuwarsu da ta al’umma gaba ɗaya,” in ji shi.

Sanatan ya kuma bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ƙoƙarinta wajen tallafa wa yayan talakawa, amma ya ce akwai bukatar masu hannu da shuni su taka rawa wajen inganta harkar ilimi.

“Gwamnati ba za ta iya yin komai ita kaɗai ba. Dole ne masu hali su fito su tallafa. Wannan dalilin ya sa na kafa wannan tsari domin ilimantar da matasanmu,” in ji Sanata Barau.

Sanata Barau ya bayyana cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban kowace kasa, inda ya ce: “A duk duniya, babu abinda yake samar da ci gaban tattalin arziki kamar dan Adam mai ilimi da horo. Idan muna da matasa masu ilimi a bangarorin kimiyya da fasaha, to Najeriya za ta amfana matuƙa.”

Sanatan ya kuma ja hankalin matasan da za su amfana da wannan dama cewa su yi kokari wajen kafa nasu masana’antu domin samar da ayyukan yi.

“Muna son ganin matasanmu suna kafa kamfanoni, su zama masu daukar ma’aikata maimakon su jira neman aiki. Za mu tabbatar da cewa bayan sun kammala karatun, za su sami tallafi domin kafa kamfanonin su,” in ji shi.

Wannan shiri na tallafin karatu zai zama tsarin shekara-shekara, kuma Sanata Barau ya tabbatar da cewa za a ci gaba da gudanar da shi.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da shirin, Salisu Auwal Musa daga karamar hukumar Nasarawa, ya bayyana farin cikinsa da damar da aka bashi.

Ya ce:”Ban taɓa fita daga Najeriya ba, amma yanzu ga ni zan je India don yin digiri na biyu a fannin kimiyyar mutumi-mutumi (Robotics Science).

“Wannan dama babbar nasara ce a gare ni da iyalina, kuma na gode wa Sanata Barau bisa wannan taimako.”

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp