fidelitybank

Sanata Barau ya dauki nauyin Matasa 70 su karo karatu a kasar Indiya

Date:

Sanata Barau Jibrin, mai wakiltar Kano ta Arewa, ya ɗauki nauyin matasa 70 daga jihar Kano don yin karatun digiri na biyu a kasar India.

Wannan shiri na tallafin karatu ya mayar da hankali ne kan bangarorin kimiyya da fasaha, musamman Fasahar zamani (Artificial Intelligence), Kimiyyar Mutumi-mutumi (Robotics), da sauran fannoni na zamani.

Da yake magana a lokacin da yake raka matasan zuwa filin jirgin sama, Sanata Barau ya bayyana cewa manufar wannan shiri shi ne tallafa wa matasa daga gidajen talakawa domin samun ilimin da zai taimakesu da al’ummar baki ɗaya.

“Mun san cewa babban kalubalen Arewa shine rashin ilimi. Yawan matasa albarka ne, amma wannan albarka ba za ta amfani kasa ba sai an basu ilimi mai inganci. Saboda haka, na ɗauki nauyin tura matasa 70 zuwa India domin samun ilimin da zai canza rayuwarsu da ta al’umma gaba ɗaya,” in ji shi.

Sanatan ya kuma bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ƙoƙarinta wajen tallafa wa yayan talakawa, amma ya ce akwai bukatar masu hannu da shuni su taka rawa wajen inganta harkar ilimi.

“Gwamnati ba za ta iya yin komai ita kaɗai ba. Dole ne masu hali su fito su tallafa. Wannan dalilin ya sa na kafa wannan tsari domin ilimantar da matasanmu,” in ji Sanata Barau.

Sanata Barau ya bayyana cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban kowace kasa, inda ya ce: “A duk duniya, babu abinda yake samar da ci gaban tattalin arziki kamar dan Adam mai ilimi da horo. Idan muna da matasa masu ilimi a bangarorin kimiyya da fasaha, to Najeriya za ta amfana matuƙa.”

Sanatan ya kuma ja hankalin matasan da za su amfana da wannan dama cewa su yi kokari wajen kafa nasu masana’antu domin samar da ayyukan yi.

“Muna son ganin matasanmu suna kafa kamfanoni, su zama masu daukar ma’aikata maimakon su jira neman aiki. Za mu tabbatar da cewa bayan sun kammala karatun, za su sami tallafi domin kafa kamfanonin su,” in ji shi.

Wannan shiri na tallafin karatu zai zama tsarin shekara-shekara, kuma Sanata Barau ya tabbatar da cewa za a ci gaba da gudanar da shi.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da shirin, Salisu Auwal Musa daga karamar hukumar Nasarawa, ya bayyana farin cikinsa da damar da aka bashi.

Ya ce:”Ban taɓa fita daga Najeriya ba, amma yanzu ga ni zan je India don yin digiri na biyu a fannin kimiyyar mutumi-mutumi (Robotics Science).

“Wannan dama babbar nasara ce a gare ni da iyalina, kuma na gode wa Sanata Barau bisa wannan taimako.”

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp