Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Ahmed Yerima, ya bi sahun masu neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki.
Ya bayyana aniyar sa a fadar shugaban kasa dake Abuja bayan ya gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Yerima, yayin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban kasa bayan ganawarsa da shugaban kasar, Yerima ya ce zai kara inganta kokarin gwamnatin Buhari.
Yerima, ya ce, zai mayar da hankali ne kan muhimman abubuwa guda uku da suka hada da rashin tsaro, fatara da jahilci, ya kara da cewa nan take zai zabo ‘yan takarar jam’iyyar APC da nuna sha’awa.