Sa’o’i 24 bayan tabbatar da sauya shekar sa zuwa jam’iyyar PDP, Sanata Adamu Alieru, ya musanta cewa ya sauya sheka.
A cewar kakakinsa, Abdullahi Zuru tun da farko ya tabbatar da sauya shekarsa zuwa wata jam’iyya ya ce ‘yan sa’o’i kadan bayan wallafa labarin wani ci gaba ya kai kusan rabin yunkurin sauya sheka “shugabana yana tattaunawa kan mataki na gaba.
Tun da farko Alieru ya fice daga takarar ne bisa zargin sauya wakilai da gwamnan jihar Atiku Bagudu ya yi kafin zaben fidda gwani, ya kara da cewa nan ba da jimawa ba zai yanke shawara amma a halin yanzu Alieru yana nan a APC.