Shugaba Joe Biden na Amurka, ya kira sammacin kama firaministan Isra’ila da kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta ba da da abin takaici.
ICC ta ce ta bayar da sammacin Benyamin Netanyahu kan zargin aikata laifukan yaƙi a Gaza.
Tuni ‘yan siyasa a Isra’ila suka fara martani kan hukuncin, ciki har da tsohon firaministan ƙasar, Naftali Benneth, wanda ya ce an ”gina ilahirin sammacin a kan ƙarya”,
”Wannan abin dariya ne ma, za mu maida martani, ba za mu zuba ido haka nan a cuce mu ba”, in ji Mista Benneth.
Da wannan sammacin na kotun ICC ƙasashe mambobin kotun na da damar kamawa tare da tsare Mista Netanyahu idan ya shiga ƙasashensu.