fidelitybank

Samar da shugabanci na gari ne zai kawo wa Afrika cigaba – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya kuma shugaban ƙungiyar Ecowas, Bola Tinubu ya yi kira ga shugabannin ƙasashen Afirka ta Yamma da su fifita samar da shugabanci nagari ga mutanen yankin, saboda a cewarsa shi ne kawai hanyar inganta da ci gaban tattalin arzikin yankin.

Yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron ƙungiyar da aka gudanar a birnin Abuja na Najeriya, shugaba Tinubu ya ce tsarin shugabanci nagari ne zai magance tarin matsalolin da al’umomin ƙasashen yankin ke fama da su, kamar inganta rayuwa da samar da kyakkyawan yanayin samar da gaba mai ɗorewa.

Shugaban na Najeriya ya ce samar da shugabanci nagari ne zai iya magance matsalolin yunwa da talauci da rashin tsaro da rashin aikin yi da rashin daidaito da sauran matsalolin da suka yi wa yankin katutu.

”Ya kamata mu samu nasarar magance wasu matsalolin juyin mulkin soji a yankinmu”. in ji Tinubu.

Ya ci gaba da cewa lokaci ya yi da za a ƙarfafa tsarin dimokraɗiyya da mutuntu haƙƙoƙin talakawan yankin na zaɓar shugabannin da suke so.

“Yankinmu ya amince da ɗaukar tsaurara matakai ga duk wata ƙasa da ke cikin ƙungiyarmu da ta yi yunƙurin kawar da halastacciyar gwamnatin da talakawa suka zaɓa”, in ji Tinubu.

Yayin da takunkuman da za mu ɗauka ga ƙasa za su haifar da wasu matsalolin, yana da muhimmanci mu fahimci cewa muna koƙari ne wajen kare wa talakawa haƙƙoƙinsu tare da mutunta ‘yancinsu.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp