Shugaban Najeriya kuma shugaban ƙungiyar Ecowas, Bola Tinubu ya yi kira ga shugabannin ƙasashen Afirka ta Yamma da su fifita samar da shugabanci nagari ga mutanen yankin, saboda a cewarsa shi ne kawai hanyar inganta da ci gaban tattalin arzikin yankin.
Yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron ƙungiyar da aka gudanar a birnin Abuja na Najeriya, shugaba Tinubu ya ce tsarin shugabanci nagari ne zai magance tarin matsalolin da al’umomin ƙasashen yankin ke fama da su, kamar inganta rayuwa da samar da kyakkyawan yanayin samar da gaba mai ɗorewa.
Shugaban na Najeriya ya ce samar da shugabanci nagari ne zai iya magance matsalolin yunwa da talauci da rashin tsaro da rashin aikin yi da rashin daidaito da sauran matsalolin da suka yi wa yankin katutu.
”Ya kamata mu samu nasarar magance wasu matsalolin juyin mulkin soji a yankinmu”. in ji Tinubu.
Ya ci gaba da cewa lokaci ya yi da za a ƙarfafa tsarin dimokraɗiyya da mutuntu haƙƙoƙin talakawan yankin na zaɓar shugabannin da suke so.
“Yankinmu ya amince da ɗaukar tsaurara matakai ga duk wata ƙasa da ke cikin ƙungiyarmu da ta yi yunƙurin kawar da halastacciyar gwamnatin da talakawa suka zaɓa”, in ji Tinubu.
Yayin da takunkuman da za mu ɗauka ga ƙasa za su haifar da wasu matsalolin, yana da muhimmanci mu fahimci cewa muna koƙari ne wajen kare wa talakawa haƙƙoƙinsu tare da mutunta ‘yancinsu.