fidelitybank

Sama da yara 300 ƴan bindiga suka kore su daga makaranta a Jihar Katsina – Sa’ad

Date:

Akalla yara 3,000 ne wasu ‘yan bindiga suka kora daga makaranta a wasu kauyukan karamar hukumar Jibia ta jihar Katsina.

Malam Sa’ad Salihu, Shugaban sansanin ‘yan gudun hijirar ne ya bayyana hakan a wata ziyara da manema labarai suka kai yankin ranar Litinin.

Salisu, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Cigaban Matasan Shimfida, ya ce, wasu daga cikin yaran suna makaranta lokacin da al’ummar yankin suka fara gudu daga yankin saboda ‘yan fashi.

Ya bayyana cewa, da yawa daga cikin ‘yan gudun hijirar, wadanda a halin yanzu suke makarantar sakandiren ‘yan mata ta gwamnati, Jibia, sun fito ne daga al’ummomin Kwari, Zango, Shimfida, Tsauni, Far Faru, Tsambe da Gurbin Magariya.

A cewarsa, babban koma baya ne a fannin ilimi, sakamakon yawan yaran da barayin suka kore su daga makaranta, inda ya ce, sama da ‘yan gudun hijira 15,000 ne a sansanin.

“Akalla mata da kananan yara 23 ne suka mutu a sansanin a cikin watanni hudu, ko dai sakamakon hauhawar jini ko damuwa, yayin da mata 35 suka haihu.

“Sama da yara 3,000 da ke sansanin a halin yanzu ba su iya samun ilimi a halin yanzu.”

“Daga al’ummar Shimfida kadai, muna da mutane 8,000 da ke wannan sansanin; Al’ummar Far Faru, sama da 7,000 da kusan 200 sun fito ne daga al’ummar Zango.

“Wasu daga cikin ‘yan gudun hijirar na can a wasu sassan Jamhuriyar Nijar; baki daya, kimanin mutane 20,000 ne ‘yan fashin suka kori daga yankunansu.

“Amma ba dukkanmu muke kwana a nan ba saboda rashin katifu da ruwa da tabarmi da gidan sauro. Wasu daga cikin matan kan je gidajen ‘yan uwansu su kwana.” Salihu yace.

Salihu ya bayyana cewa, sun yi watsi da gonakinsu kuma ba su da wata hanya domin ‘yan bindiga sun kwace filayen.

Ya kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta yi duk mai yiwuwa wajen farfado da tsaro a cikin al’ummarsu domin su dawo su ci gaba da rayuwarsu ta yau da kullum.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp