Majalisar Dinkin Duniya ta ce, sama da ‘yan Ukraine miliyan uku ne suka tsere daga kasar, kuma kusan rabinsu yara ne.
Hukumar kula da kananan yara ta Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ta ce – kowace daƙiƙa – yaro ɗaya a Ukraine na zama ɗan gudun hijira.
UNICEF ta ce akwai tsananin buƙatar ayyukan kare yara ƙananan ‘yan gudun hijira, musamman wadanda aka rabu da iyayensu domin sun fi fuskantar cin zarafi da kuma safararsu.
Wannan shi ne matsalar ‘yan gudun hijira mafi girma a Turai tun bayan yakin duniya na biyu kuma matsalar ba ta nuna alamun raguwa ba.