fidelitybank

Sama da mutane miliyan 20 na fama da ciwon Hanta a Najeriya

Date:

Yau ce ranar yaƙi da cutar ciwon hanta ta duniya, inda ake gangamin wayar da kai don kawar da cutar da kuma ƙarfafa gwiwar al’umma su rika yin gwaji don gano mutum yana dauke da cutar ko akasin haka.

Bincike ya nuna cewa cutar hanta nau’in Hepatitis B wadda aka fi samun ta a yankin Afrika, ta kasance mafi haɗari cikin nau’o’in cutar.

Miliyoyin mutane ne ke harbuwa da cutar duk shekara ba tare da sun sani ba, abin da ya sa ake ta kiraye-kiraye ga jama’a su riƙa yin gwaji a kai-a kai.

Likitoci sun bayyana cewa akwai cutukan hanta kusan kashi biyar da ake kamuwa da su walau ta hanyar shan gurɓataccen ruwa da abinci ko shan ƙwayoyi barkatai ko ta hanyar da aka bai wa mutum jinin da bai dace ba.

Likitoci na kallon cutar hanta a matsayin shu’uma saboda yadda take cin ƙarfin ɗan’adam kafin a gano ta. Wani ƙwararren likita a Najeriya,farfesa Musa Muhammad Borodo, ya ce cutar ta yi yawa a ƙasar, “Mutane biliyan biyu ke fama da cutar ciwon hanta, yayin da a Najeriya mutane sama da miliyan 20 ke fama da cutar”.

Ya ce “Alamomin cutar sun haɗa da, sauyin launin ido zuwa kalar rawaya, zazzaɓi, da amai, sai dai idan cutar ta yi ƙamari tana haifar da aman jini, da kunburun ciki da ƙafafu. Kuma idan aka yi rashin sa’a tana shafar ƙoda ko ta haddasa cutar kansa.”

Ciwon hanta na cikin manyan cutuka masu haɗari da ke addabar jama’a, abin da ya sa Hukumar Lafiya ta Duniya ta haɗa gangami don kawar da ita nan da shekara ta 2030, ta hanyar yi wa jama’a gwaji da kuma riga-kafi musamman ga ƙananan yara. In ji BBC.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp