Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce adadin wadanda suka mutu a yaƙin da ake yi ya kai 11,078.
Wannan ya haɗa da yara 4,506 da mata sama da 3,000 kamar yadda ma’aikatar ta wallafa a shafin Telegram.
Sama da mutum 27,000 ne suka jikkata, in ji sanarwar.
Idan aka kwatanta, Majaliasar Dinkin Duniya ta ce kimanin mutum 5,400 ne aka kashe a Gaza a duk fadan da Isra’ila ta yi a baya da Hamas tun bayan da ta karɓe ikon yankin a shekara ta 2007.
A baya dai Amurka da Isra’ila sun ce ya kamata a yi taka-tsantsan da alƙaluman ma’aikatar da Hamas ke gudanarwa, amma a baya Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce alkaluman na da sahihanci.