Ƙungiyar kare haƙƙin dan adam ta Amnesty International, ta bayyana cewa sama da masu zanga-zangar tsadar rayuwa 1,000 ne ke tsare a hannun hukumomin Najeriya sakamakon shiga zanga-zangar ta baya bayan nan.
Zanga-zangar wadda aka gudanar tsakanin ranakun 1 zuwa 10 ga watan Agusta ta rikiɗe zuwa tarzoma a wasu sassan ƙasar, inda aka samu rahotannin sace-sace da lalata kadarorin gwamnati a wasu jihohi.
Hukumomin tsaro a Najeriyar sun ce sun kama mutane da dama da ake zargi da hannu a yamutsin.
To sai dai a cewar kungiyar ta Amnesty International, mutanen da aka kama yan ba ruwana ne.
Malam Isa Sanusi, daraktan kungiyar a Najeriya, ya ce a kama mutane mutum 632 a Jihar Kano, yayin da kuma a Sokoto an kama mutane za su kai 109 sannan kuma a Jihar Borno an kama mutum sama da 100.
“A Bauchi ma an kama mutane sannan kuma mun sami labarin cewa Kaduna ma an kama mutane za su kai 70, a Katsina ma mutum 70 aka kama.” in ji daraktan.
“To, mutanen dai suna rarrabe ne a duka jihohi, har yanzu ba mu gama ƙididdigewa ba amma zuwa yanzu ƙididdigar da muka samu kan mutanen da aka kama sun fi 100.” daraktan ta ƙara da cewa.
Daraktan ya kuma ce “a duk lokacin da aka yi irin wannan zanga-zangar, muna sane da cewa ana yin kame na kan mai uwa-dawabi sannan ana kama mutanen da suak yi laifi da waɗanda basu yi laifi ba inda a ƙarshe waɗanda zanga-zangar suka shiga ba tare da aikata laifin komai ba, sai a nemi wani laifi a laƙa masu wanda ba su aikata ba.”
“To kuma muna da bayanin cewa akasarin mutanen da aka kama, babu wani laifin da suka aikata, kawai zanga-zanagar suka shiga kuma aka kama su.”