Tsohon mai taimaka wa a kafafen yada labarai, kuma Darakta Janar kan harkokin yada labarai da sadarwa na gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, Salihu Tanko Yakasai, ya bayyana ficewarsa daga jamâiyyar APC.
Ganduje ya sauke Salihu Tanko Yakasai daga mukaminsa, bayan ya caccaki gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.
A wani taron manema labarai a ranar Litinin, Yakasai ya ce, ya daina zama dan jamâiyya mai mulki a ranar 21 ga Maris, 2022. In ji Daily Trust.
Ya ce, “Na kasance dan jam’iyyar APC a Najeriya tun kafuwarta, kusan shekaru goma da suka wuce, dai dai a watan Fabrairun 2013.”
âAbin takaici, da amanar da muka baiwa jamâiyyar APC (gwamnati da kuma jamâiyyar) sau biyu kenan (waâadi na daya da na biyu) duk an ci amanar mutane, abubuwa sun zama mafi muni a cikin wa’adi na biyu. Fa’idar shakkun da muka baiwa jam’iyyar a zangon farko ya gushe yayin da muka kara zurfafa zuwa wa’adi na biyu, zan kuma sake tunani da tuntuba domin sanin makomata” in ji shi.
Ya kuma yabawa Ganduje bisa yadda ya bashi damar yi wa gwamnatinsa hidima sama da shekaru biyar