A ranar Talatar nan 3 ga watan Mayu ne, Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, yake fara ziyarar kwanaki biyu a Najeriya.
A yayin ziyarar tasa, babban Jami’in na Majalisar Dinkin Duniya, zai kai ziyara jihar Borno, inda zai gana da Gwamna Babagana Umara Zulum, da kuma iyalan mutanen da rikicin Boko Haram ya yi sanadin rasa rayukansu.
Kazalika Sakatare Janar din zai gana da shugabannin addinai da na kungiyoyin mata da matasa da kuma shugabanin kamfanoni masu zaman kansu.
Baya ga wadannan mutane da zai gana da su, zai kuma gana da jami’an difilomasiyya da ma wadanda ke sansanonin Æ´an gudun hijra a jihar Borno.