Sakataren gwamnatin jihar Ebonyi, Kenneth Ugbala, a ranar Alhamis ya bayyana matakinsa na yin murabus daga cikin tawagar Gwamna Dave Umahi tare da cimma burinsa na zama wakilin al’ummar Ebonyi ta tsakiya a majalisar wakilai ta kasa ta 10.
Rahotanni na cewa, Ugbala ya bayyana hakan ne a hukumance ga manema labarai, bayan wata ganawar sirri da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC reshen jihar Ebonyi a sakatariyar jam’iyyar da ke Abakaliki, babban birnin jihar.
Ya ce, “Na zo nan ne domin in tuntubi kwamitin gudanarwa na jam’iyyarmu na Jiha da kuma neman amincewarsu da goyon bayansu don tsayawa takarar Sanatan Ebonyi ta Tsakiya a 2023.
“Kun san jam’iyyar siyasa wata kafa ce da za ku iya shiga cikin shugabanci. Kuma kafin a dauki kowane mataki, ya zama dole a tuntubi shugabannin jam’iyyar don neman amincewarsu. Shi ya sa nake nan,” inji shi.
A halin yanzu, takarar Gwamna Umahi na takarar shugaban kasa a 2023, har yanzu yana nan daram. A cewar jiga-jigan jam’iyyar APC.