Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, ya gayyaci kungiyoyin kwadago zuwa wani taron gaggawa sakamakon yajin aikin da suke yi a fadin kasar.
Kwamared Festus Osifo, shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta Najeriya ne ya tabbatar wa da jaridar The Nation taron a ranar Litinin.
A cewarsa, shugabannin kwadagon da suka hada da kungiyar kwadago ta Najeriya NLC da TUC sun nufi ofishin SGF domin taron.