fidelitybank

Sakamakon Kotun Ƙoli abun takaici ne a wajen ƴan Najeriya – PDP

Date:

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya, ta ce, hukuncin Kotun Koli a kan korafin da ta shigar tare da dan takararta Atiku Abubakar, a kan nasarar zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu, babban abin tayar da hankali ne.

Ta ce ‘yan Najeriya har yanzu sun kasa fahimtar yadda kotun koli ta lamunci manyan batutuwan yin jabun takardu da tafka karya da shaidar zur, bisa doron rashin cika ka’idojin shigar da kara.

Kotun dai ta yanke hukuncin da ya tabbatar da nasarar zaben Tinubu a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

PDP ta ce ita, da mafi yawan al’ummar Najeriya sun kadu kuma sun ji takaici tare da nuna damuwa a kan tunanin Kotun Kolin, wanda jam’iyyar adawar ta ce ta yi imani ya saba da tanade-tanaden tsarin mulkin Najeriya da kundin dokokin zaben kasar.

Sanarwar da sakataren yada labaran PDP na kasa, Onarabul Debo Ologunagba ya fitar, babbar jam’iyyar adawar ta jaddada cewa wani abin takaici ne a ce kotun koli ta gaza dabbaka tanade-tanaden doka.

A maimakon haka, sai ta yi watsi da kyakkyawan zaton mafi yawan al’ummar Najeriya wadanda ke kallonta a matsayin gidan samun adalci ta hanyar yanke hukunci a kan batun da ya yi la’akari da dokoki da al’amura na gaskiya a cikin wannan shari’a.

Ta ce da gaske ‘yan Najeriya sun yi tsammanin kotun koli za ta tabbatar kuma ta kare tanade-tanaden tsarin mulkin 1999 wadanda suka fayyace karara batun cancantar dan takara da sharadi mafi karanci da ake bukatar cikawa kafin a ayyana mutum a matsayin wanda ya yi nasara a zaben shugaban kasar Najeriya.

“Musamman la’akari da bukatar doka ta cin kashi 25 na kuri’un da aka kada a birnin Abuja da kuma batutuwan da suka keta dokoki da tsare-tsaren zabe.”

PDP dai ta ci gaba da zargin jam’iyyar APC mai mulki da tafka almundahana da jirkita sakamakon zabe.

Ta kuma yi ikirarin cewa hukuncin kamar yadda shaida ta bayyana, ya sanyaya kwarin gwiwar da ‘yan Najeriya ke da shi ga bangaren shari’a, musamman a matsayinta kotun koli na madafar karshe ga talaka.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp