Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta kasa JAMB, ta ce, sakamakon kashin farko na wadanda suka rubuta jarrabawar a ranakun Juma’a da Asabar za su fito ne a mako mai zuwa.
Shugaban JAMB, hulda da jama’a da kuma ladabi (PAP), Dakta Fabian Benjamin, wanda ya tabbatar wa jaridar The Nation a ranar Asabar.
Sai dai an tattaro cewa, hukumar za ta fara fitar da sakamakon ne daga ranar Litinin ko Talata.
Benjamin ya ce, duba sakamakon jarabawar UTME da na shiga kai tsaye zai bi irin tsarin da hukumar ta dauka a bara.
Wani jami’in hukumar ya yi watsi da batun sauya jadawalin jarabawar ga wasu ɗalibai da suka kasa yin jarrabawar UTME, sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi a Legas da wasu manyan biranen kasar.
Jami’in hukumar ta JAMB ya ce, ya sabawa tsarin hukumar ta sake sanya jadawalin jarrabawar wasu a lokacin da wasu suka yi jarrabawar a gari daya ko kuma cibiya.
Jami’in ya kara da cewa, ɗaliban da suka fuskanci kalubalen na’ura ne kawai za su sake jarabawar, sakamakon cibiyoyinsu ne kawai za su samu damar sake jarabawar.
Majiyar ta ce: “Ba batun ruwan sama ba ne domin wasu sun rubuta. Haka Legas ta kasance. Ana ruwan sama, wasu sun zo rubuta jarrabawar.
“Tsarin da muke yi shi ne, muddin wasu sun rubuta wannan jarrabawar ba za mu iya sake sanya wa kowane dan ɗalibi lokaci ba.