fidelitybank

Sakamakon jarabawa zai fito a makon gobe – JAMB

Date:

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta kasa JAMB, ta ce, sakamakon kashin farko na wadanda suka rubuta jarrabawar a ranakun Juma’a da Asabar za su fito ne a mako mai zuwa.

Shugaban JAMB, hulda da jama’a da kuma ladabi (PAP), Dakta Fabian Benjamin, wanda ya tabbatar wa jaridar The Nation a ranar Asabar.

Sai dai an tattaro cewa, hukumar za ta fara fitar da sakamakon ne daga ranar Litinin ko Talata.

Benjamin ya ce, duba sakamakon jarabawar UTME da na shiga kai tsaye zai bi irin tsarin da hukumar ta dauka a bara.

Wani jami’in hukumar ya yi watsi da batun sauya jadawalin jarabawar ga wasu ɗalibai da suka kasa yin jarrabawar UTME, sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi a Legas da wasu manyan biranen kasar.

Jami’in hukumar ta JAMB ya ce, ya sabawa tsarin hukumar ta sake sanya jadawalin jarrabawar wasu a lokacin da wasu suka yi jarrabawar a gari daya ko kuma cibiya.

Jami’in ya kara da cewa, ɗaliban da suka fuskanci kalubalen na’ura ne kawai za su sake jarabawar, sakamakon cibiyoyinsu ne kawai za su samu damar sake jarabawar.

Majiyar ta ce: “Ba batun ruwan sama ba ne domin wasu sun rubuta. Haka Legas ta kasance. Ana ruwan sama, wasu sun zo rubuta jarrabawar.

“Tsarin da muke yi shi ne, muddin wasu sun rubuta wannan jarrabawar ba za mu iya sake sanya wa kowane dan ɗalibi lokaci ba.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp