fidelitybank

Sakamakon dukan likita Asibiti ya sanya suka hana gawa

Date:

Hukumomin asibitin koyarwa da ke Ilorin a jihar Kwara ta ƙi bayar da gawar wani mutum da ya mutu tare da kama ɗaya daga cikin ‘yan uwan mamacin bisa zargin lakaɗa wa wani likitan asibitin duka.

Jaridar Punch  ta ruwaito cewa, uku daga cikin ‘yan uwan mamacin mai suna Alhaji Saliu ne suka doki wani likita a sashen kula da masu buƙatar kulawar gaggawa na asibitin.

Saboda abin da suka kira ‘rashin kula’ da lilitocin suka nuna musu lamarin da a cewarsu ya sa ɗan uwan nasu ya mutu.

Lamarin ya faru ne jim kaɗan bayan rasuwar ɗan uwan nasu wanda ke fama da cutar sankarar jini.

Ɗaya daga cikin ‘yan uwan mamacin ya ce asibitin ya hana su gawar mamacin saboda faruwar lamarin.

Ya ƙara da cewa sun kai ɗan uwan nasu sashen kula da masu buƙatar kulawar gaggawa na asibitin wajen ƙarfe biyar na asubahin ranar Talata, kuma babu likitan da ya zo kan ɗan uwan nasu duk kuwa da irin roƙon da suka riƙa yi wa likitocin.

Shugabar ƙungiyar likitoci reshen asibitin Mrs Mrs. Elizabeth Ajiboye ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa ”gamayyar ƙungiyar likitoci ta ƙasar ne suka umarci hukumomin asibitin da kada su bayar da gawar mamacin har sai an kama tare da gurfanar da mutanen da suka daki likitan a gaban kotu”.

Daga ƙarshe ta shawarci al’umma da su guji ɗabi’ar cin zarafin ma’aikatan lafiya.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...
X whatsapp