fidelitybank

Sai Sojoji su fatattaki ƴanbindiga daga dazuka kafin a samu zaman lafiya – Ganduje

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya ce, dole sojoji su fatattaki ƴanbindiga su ƙwace dazukan Najeriya domin kawo ƙarshen rashin tsaro.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ta’aziyar jaje ga Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago bisa rasuwar gomman mutane a sanadiyar gobarar fashewar tanka a jihar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

A wata sanarwa da sakataren watsa labaran jam’iyyar APC na ƙasa, Edwin Olofu ya fitar a ranar Alhamis a Abuja, Ganduje ya ce akwai buƙatar a ƙara ƙaimi, musamman wajen fatattakar ƴanbindiga daga dazukan Najeriya domin kawo ƙarshen yaƙin harkokin ƴanbindiga a ƙasar.

“Hanyar da za a magance wannan matsalar ita ce a ƙwace dazuka saboda ƴanbindigar nan a cikin dazuka suke zama. Me ya sa muka koma muna jira su kawo hari, kafin mu tare su? lokacin da nake gwamna, kira na yi ga gwamnatin tarayya da ta zuba sojoji a dajin Falgore, wanda hakan ya sa aka kafa sansanin horar da sojoji.

“Tun daga lokacin ne aka fatattaki ƴanbindiga daga dajin, kuma Kano ta samu zaman lafiya,” in ji Ganduje.

Da yake mayar da martani, Gwamna Bago ya yi godiya bisa ziyarar jajen, sannan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gyare titin Suleja-Minna domin rage yawaitar haɗura.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp